Akalla mata shida ne suka mutu a kasar Poland bayan da likitoci suka ki zubar masu da ciki saboda hukuncin da kotun tsarin mulkin kasar ta yanke kan zubar da ciki.
Dr Vincent Isegbe, babban darkta a hukumar kula da dabbobi da tsirrai a Najeriya (NAQS), shi ne ya saka hannu a madadin Najeriya inda Dr Javier Arriaga ya wakilci Mexico a birnin Mexico City.
A ci gaba da samun nasarorin da Najeriya ta samu a yakin da take yi da ta'addanci, kasa da kasashe bakwai na Afirka ne ke neman shiga cikin manhajar horar da Cibiyar Nazarin Tsaro ta NISS da ke Abuja, bangaren horar da jami'an tsaron farin kaya na Najeriya DSS. .
Rundunar ‘yan sanda a jihar Kwara ta kama wasu mutane takwas da ake zargin masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, tare da gano tireloli uku na duwatsun marmara a karamar hukumar Patigi da ke jihar.
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party, NNPP, Rabi’u Kwankwaso, ya sha alwashin bayar da hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta Afirka ta Yamma, (WAEC), Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB da kuma National Examination Council (NECO) kyauta ga daukacin yaran Najeriya.
Shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mohamud ya bayyana cewa, tagwayen bama-bamai da suka fashe a cikin wata mota da aka kai kan wani gini na ma’aikatar ilimin kasar, ya hallaka mutane a kalla 100 kana wasu sama da mutum 300 sun jikkata.
Maharin, wani farar fata ne , ya nufi cibiyar a cikin wata farar motar motsa jiki ta SEAT. Ya fito ya jefa bama-baman fetur guda uku, inji wani mai daukar hoto na kamfanin dillancin labarai.