Shugaba Volodymyr Zelensky na Ukraine ya ce kashi 10 cikin 100 na al’ummar kasar yanzu haka na rayuwa ba lantarki sakamakon hare-haren Rasha da suka yi illa ga turakun wutar lantarki.
Bayanai daga Togo na cewa hare-haren ta’addanci a makwafciyar kasar Burkina Faso ya yi sanadin raba mutane fiye da dubu 4 da muhallan su. Jamhuriyar Benin da Ghana da kuma Ivory Coast na fuskantar baranazar fantsamar hare-haren ta’addanci.
Kafofin yada labaran kasar Syria sun rawaito cewa, an kai hare-hare ta sama da Isra'ila ta kai a kusa da Damascus babban birnin kasar Syria, lamarin da ya kasance karo na uku cikin mako guda.
Yunkurin da sojojin Rasha suka yi na sake kai farmakin a birnin Kharkiv, inda a baya-bayan nan suka yi asarar fiye da murabba'in kilomita 8,000 (kilomita 3,088), bai yi tasiri ba. Sojojin Ukraine sun ce yanzu haka sun sake kwato matsugunai 544 a yankin, yayin da 32 kacal suka rage a mamaya.
Akalla mutane 9 aka kashe, tare da jikkata wasu 47 ranar Lahadi, a wani hari da aka kai kan wani Otal da ke birnin Kismaayo a kudancin Somalia, farmakin da kungiyar Al-Shabaab ta dauki alhakinsa.
Shugaban kasar Ukraine Volodymyr Zelensky ya bayyana cewa, kasar Rasha ta kaddamar da wani sabon kazamin hari a kan tashar makamashin Ukraine. Ya ce hare-haren sun yi nisa sosai, inda suka afkawa yankunan Ukraine a yamma, tsakiya, kudu da gabashi.
Jam’iyyar Oodua Peoples Congress (OPC) ta ce hare-haren ta’addancin da ke faruwa na iya haifar da sabon yaki a Najeriya. Kungiyar ta yi wannan gargadin ne biyo bayan makircin da 'yan ta'adda suka yi na kai hari a wasu jihohin kasar. Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (NSCDC) ta bayyana cewa kungiyar Boko Haram, ISWAP, da kungiyoyin ‘yan bindiga na shirin kai hare-hare. Suna kaiwa jihohin Katsina, Zamfara, Kaduna, Kogi, Legas da kuma babban birnin tarayya Abuja hari. OPC ta ce ‘yan ta’addan za su fuskanci turjiya mai tsauri idan suka yi yunkurin kai hari yankin Kudu maso Yamma. A wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, Sakataren Yada Labarai, Yinka Oguntimehin, ya yi Allah-wadai da sabon mamaye Owo a Jihar Ondo. Ya yi gargadin cewa hare-haren suna nuni ne ga "yakin da ke kusa da zai iya tura Najeriya ga tudun mun tsira". Kakakin ya zargi gwamnatin tarayya da “kasa yin aiki” tare da bayyana cewa kalubalen tsaro ya mamaye ta. “Shugaba Muhammadu Buhari ya kasa daidaita kalamansa da ayyuka. “Makarantar gwamnati a Abuja, jihar Nasarawa da wasu sassa na rufewa a sakamakon karuwar rashin tsaro. “Al’amarin yana kara ta’azzara inda kashe-kashe ke karuwa. Akwai bukatar gwamnonin Kudu maso Yamma su tashi cikin gaggawa tun kafin lokaci ya kure. Sanarwar ta kara da cewa "Bai kamata mu dauki barazanar 'yan ta'adda ba, dole ne mu dauki mataki a yanzu".